• English
  • Business News
Monday, June 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto and Sulaiman
3 days ago
in Rahotonni
0
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar kasa daga Arewa zuwa Kudu sun gudanar da shagalin bukin muhimmiyar ranar Babbar Sallah a cikin mummunan yanayin tabarbarewar tattalin arziki da ya hanawa bukin sallar armashi.

Bukin sallar layya na zuwa ne kwana daya bayan miliyoyin al’ummar musulmin duniya sun yi hawan Arafat, ranar da ta fi kowace rana daraja a cikin ranakun duniya.

  • Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
  • Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Sallah Babba wadda ake gudanarwa a kowace ranar 10 ga watan Zul -Hijja a fadin duniya bakidaya rana ce ta musamman da al’ummar musulmi ke yanka dabbobi domin koyi da jagoran Annabawa, manzon tsira kuma shugaban talikai, Annabi Muhammad (SAW)

Al’umma da dama da suka saba yin layya a baya, a bana suna dauke da tambarin matsaloli a fuskokin su domin kuwa layya ta gagare su a dalilin matsin tattalin arziki wanda ke da alaka da tsauraran manufofin tattalin arziki na gwamnatin Tinubu wadanda al’ummar kasa ke kokawa a kai.

Duk da gwamnatoci a dukkanin matakai sun biya albashin watan Mayu amma ma’aikata da dama ba su samu zarafin gudanar da ibadar layya ba domin albashin ba zai wadace su sayen dabbobi da abinci ba.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

An gudanar da sallah ne bayan da Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III ya bayyana ranar Juma’a 06 ga Yuni a matsayin ranar 10 ga watan Zul-Hijja 1446 a matsayin ranar sallar layya kamar yadda ya bayyana a sanarwar da shugaban kwamitin lamurran addinin musulunci kana Wazirin Sakkwato, Farfesa Sambo Wali Junaid ya sanyawa hannu.

A ra’ayin jama’a da dama ba su da halin sayen dabbobin layya da za su yanka, wasu kuwa sun bayyana cewar ko da suna da halin yin layya to ba ita ce a gaban su ba domin a cewarsu za su shiga cikin gagarumar matsala a gidajen su domin mafi yawa ba su tanadi abincin da iyalansu za su ci ba don haka sayen abinci ne mafi muhimmanci.

Talakawa da daman gaske da kanana da matsakaitan ma’aikata da kananan ‘yan kasuwa sun shaidi sallar layya a wannan shekarar a halin da suke fatar kada Allah ya maimaita domin a ta bakin su ba a taba shaidar sallah a matsin tattalin arziki irin ta wannan shekarar ba.

Tashin gwauron- zabi da dabbobin layya suka yi, hauhawar farashin abinci, tsadar man fetur da halin kuncin da jama’a ke ciki duka abubuwa ne muhimmai da suka taru suka dabaibaye sallar ta hanyar hana mata karsashi.

Gagarumar matsalar tsaro ba dare ba rana daga Borno zuwa Sakkwato, tashin bama- bamai, garkuwa da mutane da kisan gillar da ‘yan ta’adda ke yi wa al’umma ba kakkautawa sun yi matukar tasiri wajen hanawa sallah karsashi.

Rahotanni sun tabbatar da cewar tsananin tsadar da dabbobin layya suka yi ya tilastawa jama’a da dama hakura da yin layya domin abincin da za su ci yana kokarin gagarar su wanda ya zama dalilin da ire-iren wadanda suka samu kudin layya to abinci suke siya wanda shine ya fi muhimmanci.

Auwal Balarabe wani matsakaicin ma’aikaci a Abuja ya bayyana cewar wannan layya ce ta farko a tarihin rayuwarsa da aka yi ba ya da halin yanka dabba wanda a cewarsa ya shiga cikin tarihin da ba zai manta ba a dalilin matsin rayuwa.

Wasu maigidanta a Kano sun bayyana cewar ba za su wahalar da kan su sayen ragon dubu 200 zuwa 250 ba, shanu kuwa sai dubu 500 zuwa miliyan daya don haka suka hakura suka zabi sayen kaji da nama.

Mabambantan al’umma sun bayyana halin rashin da aka fuskanta a wannan shekarar da hauhawar farashin raguna da sauran dabbobin layya ya tilastawa mutane da dama hada kudade domin yin hadakar layya ta hanyar sayen babbarn sa ko saniya wadanda suka kai adadin shekaru biyu na layya.

Wani magudanci Isna’il Abubakar a Sakkwato ya bayyana cewar ragon da ya saya a 2024 a dubu 150 a yanzu sai 260, don haka da shi da makwabta hudu sun hada dubu 800 domin sayen saniya su raba.

Bincike a mabambantan kasuwannin karar dabbobi ya nuna an samu karancin masu sayen raguna, shanu da sauran nau’ukan dabbobi sama da shekarun baya kamar yadda masu sayar da raguna a Abuja, Kano, Bauchi, Kaduna, Neja, Gusau, Sakkwato da Birnin- Kebbi suka bayyanawa manema labarai.

“Ba mu taba ganin sallar da jama’a suka kasa yin tururuwar zuwa sayen dabbobi ba irin wannan shekarar, ko kadan babu ko irin rabin hada-hadar da muka saba samu a shekarun baya.”

A cewar Hassan Mahe ko kadan kasuwar dabbobi a bana ta bambanta da saura domin babu kasuwa, kuma duk da tsadar abincin dabbobi, farashin ya karu ne a dalilin hana shigowa da su daga Nijar da gwamnatin kasar ta yi wanda a kan hakan farashin dabbobin ya ninka.

Baya ga wannan matsalar tsaro wadda ta ki ci ta ki cinyewa gagarumar matsala ce wadda ta hanawa bukin sallah armashi a yankuna da dama da ke fama da matsalar tsaro a kasar nan a dalilin hare- haren ta’addanci.

Haka ma dinbin al’ummar da ke tsugune a sansanin ‘yan gudun hijira ko kadan babu maganar kayatarwar shagalin sallah ko yin layya a wajen su, hasalima ranar sallah kan tuna masu da lokutan baya da suka yi sallah cikin walwala da farin ci a muhallansu kuma a cikin iyalan su.

Kayan abinci kamar shinkafa, masara, gero, dawa, wake, fulawa, man gyada, man-ja da nau’ukan tumatur, albasa, attarugu, tattasai da sauransu sun yi matukar tsada lamarin da tsadar a kullum sai gaba-gaba take yi wanda hakan ya taimaka wajen kara rage armashin sallah domin jama’a da dama ba su da wadatar sayen kayan bukatu.

Maigidanta da dama a tattanawarsu da LEADERSHIP Hausa sun bayyana fatar samun saukin al’amurra ta yadda dabbobi da kayan abinci da na bukatu za su sauko kasa akasin shekaru biyu da suka gabata zuwa yanzu da al’amurra suka tabarbare har jama’a suka shiga cikin kunci maras misaltuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

Next Post

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Related

Tsadar rayuwa
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

2 days ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
Next Post
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

LABARAI MASU NASABA

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

June 8, 2025
Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

June 8, 2025
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

June 8, 2025
Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

June 8, 2025
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

OSZAR »