Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, reshen jihar Kano, ta kama wasu mutane 19 da ake zargi da ta’ammuli da miyagun kwayoyi a wani samame da ta kai a wasu fitattun wurare da ke jihar.
Kakakin hukumar rundunar na jihar, Sadiq Maigatari ya ce an kama wadanda ake zargin ne a wani samame da aka yi a yankunan Dorayi, Gwammanja, Zango, da Jaen a jihar.
Maigatari ya kara da cewa, rundunar ta kuma gano wasu haramtattun abubuwa da wadanda ake zargin suke amfani da su wurin aikata laifuka daban-daban.
A cewarsa, shaye-shayen miyagun kwayoyi, shi ne musabbabin da ke haifar da aikata laifuka da dama, wanda galibi ke zama sanadin tashin hankali da rikice-rikice a cikin al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp