Daga ranar 30 ga watan Mayu zuwa ranar 1 ga watan Yuni, an gudanar da taron tattaunawa na Shangri-La karo na 22 a kasar Singapore. Taron tattaunawar, wani nau’in taro ne da ya samar da dandali na karfafa mu’amala da fahimtar juna ta hanyar tattaunawa, to sai dai kasar Amurka ta mai da taron a matsayin fage na shafa wa kasar Sin bakin fenti da ma gurgunta fahimtar sassa daban daban game da hakikanin gaskiyar lamurra. A wajen taron, sakataren tsaron kasar Amurka Pete Hegseth ya yi kalaman da ba su dace ba game da kasar Sin, inda ya yada karairaiyi na wai “barazanar kasar Sin ta fannin soja”, don neman yayata manufarta ta Indo-Pasifik a matsayin wani mataki na tilas da ya dace a dauka wajen tinkarar “barazana daga kasar Sin”.
Sai dai tarihi madubi ne da ya shaida ainihin burin da Amurka ke neman cimmawa. Idan mun yi nazari a kan tarihin yadda kasar Amurka ta kafa mulkin mallaka a kasar Philippines bayan yakin da ta yi tare da kasar Spaniya a shekarar 1898, za a ga cewa ta fake ne da sunan wai “kiyaye tsaron shiyyar”. Haka nan, idan mun yi la’akari da tsarin ayyukan soja da aka kafa sakamakon yarjejeniyar hadin gwiwa da tsaro da Amurka da Japan suka cimma bayan yakin duniya na biyu, har ma da dimbin sansanonin soja da ta kafa a yankin Asiya da tekun Pasifik, za a ga shi ma har yanzu Amurka na fakewa da sunan wai kariya. Lallai Amurka ta saba fakewa da batun tsaro wajen kara karfin sojanta a duniya, sai dai a bisa akasin abin da take fada na wai “barazana daga kasar Sin”, tun bayan da kasar Sin ta gabatar da ka’idoji biyar na zaman tare cikin lumana a wajen taron Bandung yau shekaru 70 da suka wuce, kasar ta Sin ta kwance damarar sojoji kimanin miliyan, kuma ta fi daukar nauyin ayyukan kiyaye zaman lafiya na MDD, kana kullum tana dukufa a kan samar da ci gaba a sassan duniya don sa kaimin tabbatar da tsaro, a kokarin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ma ci gaba a sassan duniya.
Idan mun yi la’akari da hakikanin yanayin da muke ciki yanzu, za mu gano cewa, abin da Amurka take fada na wai “yankin Indo-Pasifik mai ‘yanci”, babakere da nuna fin karfi ne a zahiri. Yadda jiragen sojan Amurka suka sha yin zirga-zirga a tekun kudancin kasar Sin mataki ne na tsokana wadda yarjejeniyar MDD game da dokar teku ta hana, sannan duk da haka, ta bayyana rashin gamsuwarta game da “’yancin zirga-zirga” a yankin, sai dai ta manta da mene ne yake samar da tsaro, wato tsaro ga kowa a maimakon tsaro ga wata kasa kadai shi ne abin da zai iya tabbatar da tsaro, kuma ba zai yiwu ba wata kasa ta tabbatar da tsaron kanta bisa ga lalata tsaron sauran kasashe ba. Kasar Sin a nata bangaren, ta dukufa a kan gina al’umma mai makoma ta bai-daya ta fannin tsaro bisa shawarar kiyaye tsaron duniya da ta gabatar, don neman tabbatar da tsaro ga kowa cikin hadin gwiwa.
Yadda tsarin hadin gwiwar kasashen BRICS ke dada fadada, da yadda kasashen duniya ke gaggauta kaurace wa yin amfani da dalar Amurka, sai kuma yadda aka kafa cibiyar kula da harkokin shiga tsakani ta duniya, duk sun shaida sauyawar zamani da ma yadda kasashe masu tasowa suke ta kara fito da muryarsu ta neman adalci a duniya. Duk da yadda jiragen ruwan soja na Amurka ke zirga-zirga a tekun kudancin kasar Sin, yanayin da ake ciki na samun bunkasar kasa da kasa ta bai-daya ya tabbata. Bugu da kari, yadda wasu kasashe ke iya kokarin nuna fin karfi a duniya, ya shaida yadda suke dab da zuwa karshen yin haka. Duba da cewa, hadin gwiwar sassa daban daban shi ne jigon karnin da muke ciki a maimakon yaudara da fin karfi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp